Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kotu tayi watsi da bukatar soke sabbin masarautu

Published

on

Babbar kotun jihar Kano ta kori karar da masu zabar sarki na masarautar Kano suka shigar suna kalubalantar kirkirar sabbin  masarautu guda hudu da gwamnatin jihar Kano ta yi.

Da yake yanke hukunci a safiyar yau litinin, mai shari’a Ahmed Tijjani Badamasi ya kara tabbatar da hukuncin da mai shari’a Usman Na’aba ya yi a ranar 21 ga  watan Nuwamban shekarar da ta gabata na tabbatar da masarautun.

Majalisar dokoki ta Kano ta amince da dokar kafa masarautu 4

Ganduje ya sakawa dokar kikiro masarautu hannu

Kotu ta dage sauraran karar dattawan Kano kan sabbin masarautu

 

Idan za’a iya tunawa masu nada sarki a masarautar Kano wanda suka hada da Madakin Kano Hakimin Dawakin Tofa Yusuf Nabahani , da Makaman Kano kuma hakimin Wudil Abdullahi Sarki-Ibrahim da sarkin Dawaki Mai Tuta kuma hakimin Gabasawa Bello Abubakar da sarkin ban Kano hakimin Dambatta Muktar Adnan sune suka shigar da karar suna kalubalantar kirkirar sabbin masarautun.

 

 

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!