Connect with us

Labarai

An kama wanda ake zargi da sace mota a gidan gwamnatin Kano

Published

on

Ana zargin ɗaya daga cikin direbobin gidan gwamnatin Kano, da satar wata mota kirra Toyota Hilux da ake amfani da ita a ayarin mataimakin gwamnan jihar Kano.

Sai dai wasu bayanan sirri da Freedom Radio ta samu, sun tabbatar mata da cewa, an samu nasarar kama wanda ake zargi da satar motar wanda guda ne cikin direbobin fadar gwamnatin ta Kano.

Bayanan sun bayyana cewa, jami’an tsaron gidan gwamnatin sun cafke wanda ake zargi da sace motar mai suna Ya’u Gezawa a jiya Talata inda har ya ke hannun jami’an.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!