Labarai
An sace yara 1,100 cikin watanni 4 a Najeriya – Amnesty

Ƙungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International ta nuna damuwa kan karuwar sace mutane a Najeriya, inda ta ce an sace akalla mutane 1,100 tsakanin Janairu zuwa Afrilu da muke ciki, musamman a jihohin Arewa.
Daraktan kungiyar a Najeriya, Isa Sanusi, ya ce binciken da suka gudanar ya nuna cewa wadanda aka sace na fuskantar mummunan cin zarafi kamar azabtarwa, yunwa, fyaɗe da tilasta su aikata laifi.
Rahoton ya nuna manyan hare-hare a jihohin Borno, Zamfara da Kwara, inda aka sace daruruwan mutane a wurare daban-daban, ciki har da mata da kananan yara.
Amnesty ta bukaci gwamnatin Bola Tinubu da ta gaggauta ɗaukar matakan tsaro domin kare rayuka da dokiyoyin al’umma.
You must be logged in to post a comment Login