Connect with us

Labarai

Ana cigaba da bincike kan mutane 70 da ‘yan bindiga suka hallaka a Kwara

Published

on

Jami’an agajin gaggawa na Red Cross a yammacin Najeriya sun ce ana fargabar adadin mutanen da ƴan bindiga suka kashe a jihar Kwara ya kai kusan 70, biyo bayan wani mummunan hari da aka kai a ƙauyen Woro.

Red Cross ta ce har yanzu akwai mutanen da ba a gano inda suke ba tun bayan harin, inda ƴan bindigar suka kuma banka wa shaguna wuta tare da ƙone gidan sarkin gargajiya na yankin.

A wani lamari na daban, rahotanni daga jihar Katsina da ke arewacin ƙasar na nuna cewa aƙalla mutum 21 daga cikin mazauna ƙauyuka ne suka rasa rayukansu sakamakon hare-haren ƴan bindiga.

Gwamnatin Najeriya ta ce za ta ƙara ƙaimi wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma, a daidai lokacin da hare-haren kan fararen hula ke ƙaruwa a sassan arewa da tsakiyar ƙasar.

Hukumomi da jami’an tsaro sun ce ana ci gaba da bincike da kuma ƙoƙarin gano mutanen da suka ɓace, yayin da al’umma ke fatan ɗaukar matakai masu inganci domin daƙile yawaitar hare-haren ƴan bindiga.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!