Connect with us

Labarai

Ana dakon matsayar SWAN kan ƴan sanda bayan hana mambobinta daukar rahoto

Published

on

Ana dakon matakin da kungiyar manema labaran wasanni ta Najeriya SWAN reshen jihar Kano za ta ɗauka kan matakin hana ‘yan jarida mambobin ta shiga daukar bayanai da jami’an tsaro suka yi jim kadan bayan tashi daga wasan Barau FC, wanda ta yi rashin nasara da ci 1-0 har gida a hannun Warri Wolves a filin wasa na Sani Abacha da ke Kofar Mata.

Hana daukar bayanai dai Laifi ne cikin dokokin hukumar shirya gasar firimiyar Najeriya NPFL , da hakan ka iya jawo hukunci mai tsanani.

A bangare daya kuma ana ci gaba da ce ce kuce dangane da lamarin da kuma waye yake da alhakin aikata hakan tsakanin jami’an tsaron ‘yan sanda , jagororin tawagar ta Barau FC ko kuma hukumar kwallon kafa ta jihar Kano KSFA dangane da hana ‘yan jaridun gudanar da aikin su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!