Connect with us

Labarai

Ana sa ran El-rufa’i zai amsa gayyatar hukumar EFCC

Published

on

A yau Litinin ne ake sa ran tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufai, zai amsa gayyatar hukumar EFCC inda zai bayyana a ofishinta.

 

Kafar BBC ta ruwaito cewa, El-Rufai ya bayyana a jiya cewar hukumar ta aike masa da takardar gayyata zuwa ofishinta, kuma ya amince zai je ofisihin a yau Litinin.

 

Wannan lamari dai na zuwa ne bayan rahotonnin da suka bayyana cewa, jami’an tsaro sun ƙwace fasfonsa a Filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe jim kaɗan bayan dawowarsa daga kasar Masar.

 

Da ya ke yin ƙarin bayani kan wani bidiyo da ya bazu a shafukan sada zumunta, El-Rufai, ya ce ba shi ne ya yi musayar kalamai da jami’an DSS ba, sai dai su ne suka tare shi a filin jirgi suka buƙaci ya bi su ofishinsu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!