Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

APC zata daukaka kara kan shari’ar zaben gwamnan Sokoto

Published

on

Jami’yyar APC a jihar Sokoto ta bayyana cewa bata gamsu da hukuncin kotun sauraron kararrakin zabe ta gudanar a jiya ba, wacce ta kori karar da dan takarar jam’iyyar APC Ahmad Aliyu ya shigar yana kalubalantar zaben gwamna Aminu Waziri Tambuwal

 

Wannan na kunshe a wata sanarwa da Shugaban jamiyyar APC, na jihar Sokoto Alhaji Isa Acida ya fitar a yau.

 

Jamiyyar ta bayyana cewa bata amince da hukunci da kotu sauraron kararrakin ta yi ba, a cewar sa kotun ta nuna son kai da bangaranci.

 

Ya kara da cewa lauyoyin na nan na bincike kan bayanan da kotun ta fitar, sannan zasu daukaka kara a kotun da ya dace.

 

Shugaban jamiyyar ya kuma kira ga yan jamiyyar ta APC a duk fadin jihar da su kara hakuri su kuma zauna lafiya, tare da tabbabar musu da cewar jamiyyar zata yi iya kokarinta.

 

 

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!