Connect with us

Labarai

ASUU ta bai wa gwamnatin tarayya mako 2 ta magance matsalolin da ke tsakaninsu

Published

on

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya ASUU ta bai wa gwamnatin tarayya wa’adin kwana 14 domin magance matsalolin da ke tsakaninsu, ko kuma su fara yajin aikin gargadi na makonni biyu.

Wannan mataki ya biyo bayan taron gaggawa na Majalisar Zartarwa ta Ƙasa (NEC) da aka gudanar a ranar 29 ga Satumba, 2025, inda aka nazarci sakamakon kuri’ar da rassan ASUU suka kada kan batun.

ASUU ta bayyana cewa an riga an sanar da wannan ƙuduri ga Ministan Ƙwadago, Ministan Ilimi, da kuma Kungiyar Ƙwadago ta Najeriya NLC amma har yanzu babu wani ci gaba da ya cancanci a yaba da shi.

Ƙungiyar ta kuma ce, manufar ɗaukar wannan mataki ita ce tilasta wa gwamnati ta cika alkawuran da ta ɗauka tun a watan Faburairu, ciki har da aiwatar da sabunta yarjejeniyar da aka cimma.

Haka kuma ƙungiyar ta yaba wa mambobinta bisa haƙuri da fahimtar da suka nuna, tare da kiran su da su ci gaba da kasancewa cikin haɗin kai da bin umarnin shugabanninsu.

A cewar ASUU, wannan yunkuri ba don wani mutum ɗaya ba ne, sai don kare walwalar malaman jami’a da inganta tsarin jami’o’in Najeriya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!