Labarai
Atiku ya bukaci shugaba Tinubu ya ɗauki mataki mai tsauri kan matsalar tsaro

Madugun adawa a Najeriya Alhaji Atiku Abubakar, ya bukaci shugaba, Bola Ahmed Tinubu, da ya ɗauki mataki mai tsauri kan matsalar tsaro da ke addabar sassa da dama, ya na mai cewa lokaci ya yi da za a daina surutu a tunkari matsalar a aikace.
Atiku ya bayyana haka ne a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook, inda ya tuna wa shugaba Tinubu alkawarin da ya yi bayan harin da aka kai a Angwan Rukuba, inda ya ce hakan ba zai sake faruwa ba.
Haka kuma, bayyana damuwa kan halin da ake ciki a jihar Nasarawa, inda iyalai ke tserewa da ƙafafunsu sakamakon barazanar hare-hare.
Atiku Abubakar, ya jaddada cewa babban aikin gwamnati shi ne kare rayuka da dukiyoyin jama’a, tare da inganta walwalar su, don haka ya bukaci shugaban ƙasa da ya tashi tsaye wajen fuskantar ƙalubalen tsaro da ke addabar Najeriya.
You must be logged in to post a comment Login