Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ba ni ne ba a faifan bidiyon da ake yaɗawa ɗauke da bindiga ba – Ministan tsaro

Published

on

Ministan tsaron ƙasar nan Manjo Janar Bashir Salihi Magashi mai ritaya, ya musanta wani faifan bidiyon da yake yawo a kafafen sada zumunta cewa an ganshi ya shiga jirgi dauke da bindiga kirar AK-47.

Maibaiwa ministan shawara kan kafafen yada labarai Muhammad Abdulkadir ne ya bayyana hakan, ta cikin wata sanarwa da ya fitar.

Sanarwar ta ce, hotunan da kuma faifan bidiyon labari bashi da tushe ballanta makama, kawai dai masu shirin tada zaune tsaye ne suka kirkire shi.

Muhammad Abdulkadir ya tabbar da cewa, ba za a ƙyale wadanda suka kirkiri bibiyon ba, domin kuwa za a gudanar da bincike domin gano su tare da daukar mataki na gaba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!