Labarai
Ba zan yi babban shagali a bikin ranar haihuwa ta ba – Tinubu

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa zai gudanar da bikin cika shekaru 74 cikin sauƙi, la’akari da halin da ƙasa ke ciki da kuma ƙalubalen da ake fuskanta.
A cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu, ya gode wa ‘yan Nijeriya bisa addu’o’i da fatan alheri, yana mai cewa goyon bayansu na ƙara masa ƙarfi wajen jagorantar ƙasar.
Tinubu ya amince cewa sauye-sauyen da gwamnatinsa ta aiwatar sun haifar da ƙalubale, amma ya ce ana fara ganin haske a ƙarshen rami duk da matsin lamba daga rikice-rikicen duniya.
Ya buƙaci ‘yan Nijeriya da su ci gaba da haɗin kai da goyon baya, yana mai alƙawarin cewa gwamnatinsa za ta cigaba da aiki tukuru domin gina ƙasa mai ɗorewa.
You must be logged in to post a comment Login