Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Babban joji na kasa ya rantsar da sabbin alkalai

Published

on

Babban jojin kasar nan Tanko Muhammad zai rantsar da sabbin alkalai guda tamanin da biyar a gobe Alhamis wadanda za su gudanar da shari’a a kotunan karbar korafe korafen zaben cike gurbi na jihohin Edo da Ondo da sauran zabukan da za a gudanar a sassan kasar nan.

Mai magana da yawun kotun daukaka kara, Hajiya Sa’adatu Kachalla ce ta bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ta fitar a yau Laraba.

Sanarwar ta bayana cewa, za a gudanar da rantsuwar a babban dakin taro na kotun kolin kasar nan da ke birnin tarayya Abuja a gobe Alhamis.

Za dai a gudanar da zaben cike gurbi a jihar Edo a ranar sha tara ga watan Satumbar da muke ciki, yayin da na jihar Ondo za a gudanar da shi a ranar goma ga watan Oktoba mai kamawa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!