Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Abdulrashid Maina:Babbar kotun tarayya ta yi watsi da bukatar Ministan Shari’a

Published

on

Babbar kotun tarayya mai zamanta a birnin tarayya ta ki amincewa bukatar da Atoni Janar kuma ministan Shari’a Abubakar Malami ya yi, na dakatar da yunkurin majalisar Dattijai na gudanar da binciken yadda aka maida Abdulrashid Maina, tsohon shugaban kwamitin kar-ta-kwana wajen gyaran harkokin fansho bakin aiki.

Mai Shari’a Binta Nyako ta bada umarnin aikewa majalisun Dokokin kasar nan bukatar kare kansu kan kudurin na su.

Ministan Shari’ar ya kalubalanci yunkurin kwamitin majalisar Dattijan kan ayyukan gwamnati, harkokin cikin gida da kua yaki da cin hanci, na nazartar yadda aka maida Abdulrashid Maina bakin aiki , inda ya bukaci kotun ta duba shin ko majalisar da ikon gudanar da binciken.

Abubakar Malami na da ra’ayin cewa sashe na 88(1) da (2) na kundin tsarin mulkin kasar nan ya yi cikakken bayani kan ikon majalisun Dokokin kasar nan ke da shi kan wannan batu bayan da ya bada iyaka

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!