Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Bankin raya Afrika ya musanta rade-raden cewar ya baiwa kasarnan rance

Published

on

Bankin raya afurka ya musanta rade-raden da ke yawo a kafofin yada labaran kasar nan cewa ya fasa baiwa kasar nan rancen dala miliyan dari shida da ya alkawarta tun da fari.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun babbar jami’ar yada labaran bankin a kasar nan Fatima Alkali.

Sanarwar ta ruwaito mataimakin shugaban bankin mai kula da sashen samar da wutar lantarki da makamashi da kuma yanayi Amadou Hott; na musanta zargin.

A cewar Fatima Alkali ta cikin sanarwar, babu kanshin gaskiya cikin lamarin.

Sanarwar ta kara da cewa bankin raya afurka a shirye yake ya yi aiki tare da hukumomin kasar nan domin farfado da tattalin arzikin ta.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!