Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Majalisar dattawa ta bukaci kwamitinta ta yi binciken kashe-kashen jihar Benue

Published

on

Majalisar Dattawa ta bukaci kwamitinta na musamman da ke bincike kan kashe-kashen da suka faru a jihar Benue da ya gabatar da sakamakon binciken-sa a Talatar makon gobe.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da ofishin shugaban majalisar Dattawa sanata Bukola Saraki ya fitar da yammacin jiya a Abuja.

 

Sanarwar ta ce; kashe-kashen da ke faruwa a jihar Benue abin takaici ne kuma ya nuna gazawa na jami’an tsaron kasar nan.

 

A cewar sanarwar, ganin munin lamarin ya sa a watan Nuwamban bara majalisar ta Dattawa ta kafa kwamiti mai karfi karkashin jagorancin shugaban masu rinjaye Sanata Ahmed Lawan wanda aka umurci kwamitin da ya yi aiki da jami’an tsaro domin gano matsalar

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!