Connect with us

Labarai

Bauchi: Yan sanda sun ta kama wadanda da ake zargi da satar Babura

Published

on

Rundunar ’yan sandan Jihar Bauchi ta kama wasu da ake zargi da satar babura a garin Yuli.

Hakan  na cikin sanarwar da jami’in hulda da jama’a na rundunar ’yan sanda a Jihar Bauchi SP Nafiu Habib ya fitar aka rabawa manema labarai.

A cewar sa  lamarin ya faru ne bayan da wasu suka kai hari ga wani mai babur da guduma tare da kwace masa babur, inda jami’an ’yan sanda suka bi sawun su tare da kama Adamu Abubakar da ake kira Abbati mai shekaru 21 tare da kwato babur din.

Sanarwar ta ce, bincike ya kai ga kama Habibu Dauda da ake kira Commander mai shekaru 32 da ake zargi shugaban masu satar ne, tare da kama Abdurrahman Abubakar da Zubairu Garba da ake zargi sun yi yunkurin sayen babur din, inda aka kuma kwato kudi naira dubu dari hudu daga wajen su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!