Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Buhari ya amince da sabon tsarin albashi ga malaman makarantu a kasar nan

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da biyan malaman makaranta sabon tsarin albashi a kasar nan.

Shugaba Buhari ya bayyana haka a yau litinin yayin taron bikin ranar malamai ta duniya ta bana.

Buhari ya kuma kara musu wa’adin shekarun aiki daga shekara talatin da biyar zuwa shekaru arba’in a matsayin shekarun barin aiki.

Ministan ilimi Malam Adamu Adamu, wanda kuma shi ne ya wakilci shugaba Buhari yayin bikin na bana, ya ce gwamnati ta amince da karin albashin domin karfafawa malaman gwiwa wajen koyar da ilimi mai inganci.

Ana gudanar da ranar tunawa da malamai a duk ranar biyar ga watan Oktoban ko wance shekara, kuma an fara gudanarwar a shekarar 1994, domin tunawa da gudunmawar da malamai ke bayarwa a fannin ilimi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!