Labarai
Buhari ya tafi ƙasar Amurka don halartar taron Majalisar ɗinkin duniya
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2021/03/Buhari-Departs.jpg)
Da safiyar Lahadin nan shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya bar Abuja zuwa Amurka don halartar taron majalisar dinkin ɗuniya karo na 76.
Rahotonni sun tabbatar da cewa a ranar 14 ga Satumba aka fara gudanar da taron.
Taken taron a bana shi ne “Inganta rayuwa don farfaɗo wa daga cutar corona”.
Ana sa ran shugaba Buhari zai yiwa Majalisar jawabi a ranar Juma’a 24 ga Satumba kan al’amuran da suka shafi duniya baki ɗaya.
M kiai magana da yawun shugaban Femi adesina ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa a ranar Asabar.
Ya ce shugaba Buhari da mukarrabansa za su kasance cikin wasu muhimman taruka.
A cewar hadimin shugaban kasar, ana sa ran shugaba Buhari zai dawo Najeriya a ranar Lahadi 26 ga Satumba.
You must be logged in to post a comment Login