Connect with us

Labarai

Buhari ya tafi ƙasar Amurka don halartar taron Majalisar ɗinkin duniya

Published

on

Da safiyar Lahadin nan shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya bar Abuja zuwa Amurka don halartar taron majalisar dinkin ɗuniya karo na 76.

Rahotonni sun tabbatar da cewa a ranar 14 ga Satumba aka fara gudanar da taron.

Taken taron a bana shi ne “Inganta rayuwa don farfaɗo wa daga cutar corona”.

Ana sa ran shugaba Buhari zai yiwa Majalisar jawabi a ranar Juma’a 24 ga Satumba kan al’amuran da suka shafi duniya baki ɗaya.

M kiai magana da yawun shugaban Femi adesina ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa a ranar Asabar.

 

Ya ce shugaba Buhari da mukarrabansa za su kasance cikin wasu muhimman taruka.

 

A cewar hadimin shugaban kasar, ana sa ran shugaba Buhari zai dawo Najeriya a ranar Lahadi 26 ga Satumba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!