Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

CBN: zai janye kudaden da suka lalace daga hannu jama’a

Published

on

Babban bankin kasa CBN ya ce zai janye kudade da su ka lalace daga hannun jama’a, wadanda yawansu ya kai kusan naira tiriliyan takwas.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mataimakin gwamnan babban bankin kasa CBN Folashodun Shonubi da kuma daraktar kudi na babban bankin Mrs Priscilla Eleje.

Sanawar ta ce kudaden sun yi lalacewar da na’urorin ciran kudi na banki wato ATMs basa iya gudanar da hada-hada da su.

A cewar sanarwar, a gobe talata, gwamnan babban bankin kasa CBN Godwin Emefiele zai kai ziyara Lagos don kaddamar da sabon tsarin sabbin takardun kudi.

Bankin na CBN ya ce wannan wata hanya ce ta dakile lalacewar takardun naira.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!