Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

ilimi

Cin hanci da rashawa ne ya ruguza fannin ilimi a Najeriya – Dakta Bilyaminu

Published

on

Wani malami a tsangayar ilimi a jami’ar Bayero ta Kano ya ce cin hanci da rashawa na taka muhimmiyar rawa wajen tabarbarewar ilimi a Najeriya.

Dakta Bilyaminu ne ya bayyana hakan ga tashar Freedom Radio.

Ya ce cin hanci a yanzu na gaba gaba wajan durkusar da ilimi idan aka yi duba da matsalolin da a kullum ake gani a fannin ilimi.

Dakta Bilyaminu ya ce “iyaye kan goyi bayan yaransu wajen bada cin hanci ga malamai dan su samu nasara a jarabawa”.

Yana mai cewa iyaye kan biya makudan kudade don a rubutawa yaransu satar amsa musamman lokacin jarabawa kammala Sakandare ta WEAC da NECO”.

Ya kuma ce kamata yayi gwamnati ta rinka fitar da kasafin kudi mai yawa a bangaren ilimi domin inganta shi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!