Connect with us

Labarai

CISLAC ta soki afuwar da Shugaba Tinubu ta yiwa masu laifin cin hanci, fataucin miyagun kwayoyi da manyan laifuka

Published

on

Cibiyar Civil Society Legislative Advocacy Centre (CISLAC) ta nuna tsananin adawa da matakin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya dauka na bayar da afuwar shugaban kasa ga mutane 175, ciki har da wadanda aka same su da laifin fataucin miyagun kwayoyi, hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba, manyan laifuka da kuma cin hanci da rashawa.

A cikin wata sanarwa da Daraktan CISLAC kuma shugaban Transparency International Nigeria, Auwal Ibrahim Musa (Rafsanjani) ya sanyawa hannu, kungiyar ta bayyana wannan mataki a matsayin abin da bai dace da doka ba, mara da’a kuma mai bata sunan Najeriya a idon duniya.

An ce cikin jerin wadanda aka yi wa afuwa har da tsohon gwamnan Jihar Delta, James Ibori, wanda aka daure a Birtaniya, da kuma wasu da ake zargi da satar mai, garkuwa da mutane, da fataucin danyen ma’adinai, da sauran laifukan kasa da kasa. CISLAC ta ce bai dace irin wadannan mutane su ci gajiyar afuwa ba, musamman wadanda ba ma a Najeriya aka yanke musu hukunci ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!