Connect with us

Labarai

CNG ta yi Alla-wadai da shirin Shugaba Tinubu na sabbin dokokin haraji

Published

on

Gamayyar kungiyoyin Arewa watau Coalition of Northern Groups  CNG, ta yi Allah-wadai da shirin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na fara aiwatar da sabbin dokokin haraji daga farkon watan Janairun sabuwar shekarar nan ta 2026, ta na mai bayyana hakan a matsayin hari kai tsaye ga tsarin dimokiradiyya.

 

Kungiyar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a Abuja, inda ta ce akwai banbanci a tsakanin dokokin da Majalisar Dokoki ta amince da su da kuma waɗanda aka wallafa a mujallar gwamnati tana zargin cewa an yi gyare-gyare a cikin dokokin bayan Majalisa ta riga ta amince da su.

 

Kungiyar ta ƙara da cewa tilasta wa jama’a bin irin waɗannan dokoki da aka ce an canza su bayan an amince da su ya saɓa wa doka da tsarin mulki, kuma hakan na iya haifar da rashin amincewa da tsarin dimokiradiyya a zukatan al’umma.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!