Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Covid-19: Ganduje ya caccaki rahoton gwamnatin tarayya kan mace-macen Kano

Published

on

Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ya caccaki rahoton gwamnatin tarayya da ta fitar game da mace-macen da aka yi a Kano.

Maitaimakawa gwamnan kan kafafen sada zumunta, Abubakar Aminu Ibrah ne ya bayyana hakan a shafinsa na Twitter.

Cikin rahoton da kwamitin tarayya ya fitar ranar Litinin, ta bakin ministan lafiya Dakta Osagie Ehanire ya ce mutum 979 da suka mutu a wancan lokacin cikin kananan hukumomin jihar Kano takwas, na da cikakkiyar alaka da cutar COVID-19.

Dakta Ehanire ya ce shakka Babu bincikensu ya tabbatar cewa kashi 50 zuwa 60 na mace-macen a jihar Kano ya faru ne sakamakon Coronavirus wadda yanzu haka ta kama mutum fiye da dubu guda a jihar.

A watan Afrilun da ya gabata ne aka samu mace-mace a jihar Kano, abinda yafi kamari a kan masu tsawon shekaru, lamarin da aka rika zargin hakan na da alaka da cutar Coronavirus.

A wancan lokacin kwamitin karta kwana kan yaki da annobar Covid-19 na tarayya, ya danganta mace-macen da annobar Covid-19, kamar yadda binciken su ya tabbatar.

Ko da yake a wancan lokacin, gwamnatin Kano ta musanta cewa mace-macen na da alaka da annobar Covid-19, abinda ta ce shine, wasu nau’in cutuka ne da suka danganci hawan jini, ciwon sukari da dai sauran su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!