Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Cutar Deptheria ta kama mutane 557, tare da kashe 73 a Nijeriya- WHO

Published

on

Rahoton WHO ya nuna an samu ɓarkewar cutar Deptheria a jihohi 21

An fi samun yawan alkaluman waɗanda suka kamu da cutar ce a Kano

Daga ranar 14 ga watan Mayun bara zuwa 9 ga watan Afrilun bana lamarin ya fi kamari

Hukumar Lafiya ta Duniya WHO, ta ce, cutar mashaƙo watau Deptheria, ta kashe kimanin mutane 73 yayin da wasu kuma karin 557 suka kamu da cutar tun a farkon shekarar bana.

Hakan na cikin wani rahoto da hukumar ta fitar jiya Laraba, inda ta ce, an samu ɓarkewar cutar a jihohi 21 na Nijeriya.

A cewar WHO, an fi samun yawan alkaluman waɗanda suka kamu da cutar ce a jihar Kano, inda mutane dubu 1,118 suka kamu da ita.

Sai kuma jihar Yobe mai mutane 97 da Katsina mai mutane 61 da suka kamu, jihar Legas na da mutane 25 sai Sokoto mai mutane 14 da kuma Zamfara da aka samu mutane 13 da suka kamu da cutar.

Rahoton ya kuma ce, daga ranar 14 ga watan Mayun bara 2022 zuwa 9 ga watan Afrilun bana an samu alkaluman mutane dubu 1,439 da ake zargin sun kamu da cutar ta mashaƙo, inda cutar ta yi sanadiyyar rayuka 73.

Rahoton: Madeena Shehu Hausawa

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!