Connect with us

Labarai

Dakarun sojin Najeriya sun hallaka ‘yan ta’addan ISWAP a jihar Borno

Published

on

Dakarun rundunar Operation Hadin Kai, da hadin gwiwar ‘yan sa kai sun yi nasarar kashe mayakan ISWAP 17 a wani samame da suka kai da sanyi safiyar Lahadi, a jihar Borno.

Mai magana da yawun rundunar, Laftanal kanal Sani Uba, ya ce sun yi nasarar ne bayan tattara bayanan sirri a kan zirga-zirgar mayakan.

Ya ce dakarun sun tarwatsa maboyar ‘yan ta’addan kungiyar JAS da na ISWAP a kauyukan Sojiri da Kayamla na jihar Borno.

Daga cikin kayan da aka kwato daga hannun mayakan akwai babura da kayan abinci da magunguna da kayan sawa da kuma bindigogi da alburusai kala-kala.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!