Connect with us

Labarai

Dakarun sojin Najeriya sun ragargaza wani sansanin ‘yan bindiga

Published

on

Dakarun sojin ƙasar nan na rundunar 22 Armoured sun lalata wani sansanin ’yan bindiga a Karamar Hukumar Ifelodun ta Jihar Kwara.

Wannan dai na cikin wata sanarwar da Mataimakiyar Daraktar Hulɗa da Jama’a ta Rundunar, Kyaftin Maureen Ogbuka, ta fitar a ranar Juma’a.

Sanarwar ta bayyana cewa aikin ya gudana ne tsakanin ranar 23 zuwa 29 ga Janairu 2026, inda sojoji suka lalata maboyar ’yan bindiga da sansanoninsu tare da katse hanyoyin da suke amfani da su wajen jigilar kayayyaki.

Ta ƙara da cewa sojojin sun cafke wasu da ake zargi da aikata laifuka, tare da ceto mutanen da aka yi garkuwa da su daga wurare daban-daban a jihar.

Sanarwar ta kuma bayyana ce a yayin samamen, sojojin sun kashe ɗaya daga cikin ’yan bindigar, yayin da wasu suka tsere zuwa daji.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!