Connect with us

Labarai

Dalilaina na rashin komawa majalisa bayan samun umarnin Kotu- Sanata Natasha

Published

on

Sanata mai wakiltar mazaɓar Kogi ta Tsakiya,Natasha Akpoti-Uduaghan ta bayyana cewa ta jinkirta komawarta majalisa ne sakamakon  shawarwarin lauyoyi da kuma bin dokoki, duk da cewa kotu ta soke dakatarwar da aka yi mata.

Ta cikin wata  hira da ta yi da gidan talabijin na AIT, Sanata Natasha ta ce tana jiran takardar hukuncin kotu kafin ta ɗauki matakin komawa majalisar.

A baya baya nan kotu ta ce dakatarwar da aka yi mata ta yi yawa kuma ba bisa ƙa’ida aka yi ta ba.

Wani lauya daga Majalisar Dattawa, Paul Daudu mai matsayin  (SAN), ya bayyana cewa hukuncin bai ƙunshi umarnin tilasta majalisar ta dawo da ita ba.

Sanarwar dawowarta da aka shirya yi a ranar Talatar da ta gabata  ya tayar da hankula a majalisar, inda aka tsaurara tsaro tare da  kawo motocin jami’an tsaro da dama.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!