Connect with us

Labarai

EFCC ta kwato dukiyar fiye da biliyan 500 cikin shekaru biyu- Shettima

Published

on

Mataimakin Shugaban kasa, Kashim Shettima, ya bayyana cewa, Hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin kasa ta’annati EFCC, ta samu nasarar tara dukiyar da ta haura ta Naira biliyan 500 a tsawon shekaru biyu na gwamnatinsu.

Shettima, wanda ya wakilci Shugaba Bola Tinubu, ya bayyana haka ne a yayin wani taron bita da ƙara wa juna sani na alƙalai da Hukumar EFCC tare da haɗin gwiwar Hukumar Shari’a ta Najeriya NJC suka shirya a birnin tarayya Abuja.

Haka kuma, Kashim Shettima, ya buƙaci alƙalai da sauran ma’aikatan ɓangaren shari’a da su ƙara ƙaimi tare da yin aiki bisa gaskiya da adalci.

Ya kuma yi gargaɗin cewa ana fara samun matsala ne a ƙasa da zarar masu riƙe da amanar hukunci sun fara tauye haƙƙin masu haƙƙi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!