Connect with us

Labarai

El-Rufai ya zargi ofishin Ribadu da sayo guba mai matukar hadari

Published

on

Nasir El-rufa'i

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, ya zargi ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, a ƙaƙashin jagorancin Mallam Nuhu Ribadu, da sayo kimanin kilogiram 10 na wani sinadari mai haɗari da ake kira ‘thallium sulphate’, daga ƙasar Poland.

El-Rufai ya yi wannan zargin ne a cikin wata wasiƙa da ya aike wa ofishin Ribadu, inda ya ce jagororin adawar ƙasar na neman ƙarin haske game da wannan batun.

“Sinadarin thallium na da matuƙar haɗari kuma sinadari ne da ba kasafai ake samunsa ba”, kamar yadda wasiƙar El-Rufai ya bayyana cikin wasiƙar tasa.

Ya ce ya aike da wasiƙar ne domin ya nemi cikakkun bayanai kan yadda aka sayo sinadarin, yayin da ya nuna barazanar da irin wannan sinadari ka iya yi kan lafiyar al’umma.

El-Rufai ya nemi dalilin shigo da sinadarin da kuma amfanin da za a yi da shi

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!