Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Fadar shugaban kasa tayi magana kan sace hakimin Daura kuma sarkin dogarin Buhari

Published

on

Fadar shugaban kasa ta ce sace hakimin Daura kuma sirikin dogarin Buhari ya nuna cewa jami’an tsaro ba sa baiwa wani yanki kulawa ta musamman a kan wani bangare a fadin kasar nan.

Mai baiwa shugaban kasa shawara na kan kafafen yada labarai malam Garba Shehu ne ya sanar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar yau a birnin tarayya Abuja.

Ya kuma ce tuni kwamishinan yan sandan jihar Katsina Sunusi Buba ya koma zuwa birinin Daura domon ganun cewar an kubutar da hakimin daga hannun masu satar mutanen.

Ya kuma ce sace hakimin ya nunawa al’ummar kasar nan cewa matsalar garkuwa da mutane matsalace ta kasa baki daya, a cewar sa ba bu inda ake baiwa kulawa da musamman aka kuma kyale wasu.

Haka kuma ya ce wannan al’amari ya fi karfin ayyukan bata gari, a cewar sa matsala ce ta kasa baki daya da ya kamata a hada hannu wajen magance ta baki daya.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!