Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Farfesa Wole Soyinka:Kalaman kire da bata suna na barazana da bil Adama

Published

on

Farfesa Wole Soyinka ya bayyana cewa yada kalaman kire da na bata suna a Yanzu haka ya zama babbar barazana ga bil’adama kuma hakan ma ka iya tayar da yakin duniya na uku.

Farfesa Wole ya bayyana hakan ne a yayin wani taro da kafar yada labarai ta BBC ta shirya kan hanyoyin da za’a bi na magance yada kalaman kire da na bata suna da ya gudana a Abuja.

Ya kuma kara da cewa kafin kalaman kire su yi sanadiyyar barkewar yakin duniya na uku ya zama wajibi a bi duk hanyoyin da ya kamata don magance su musamman a kasa irin Najeriya.

Farfesa Wole ya kuma nuna takaicin sa kan yadda ake yawan alakanta kalaman da wasu marasa kishin kasa ke kirkirowa da a gareshi.

Inda ya buga misali da cewa ko a shekarun baya ma an alakanta wani labaran karya garshi shi, inda aka ce wai ya bayyana matar tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan a matsayin jahila.

Sannan ya kara da cewa ko a shekarar da ta gabata ma ya sha cin karo da maganganu musamman a kakafen sadarwa da ake alakan ta shi da su, wanda hakan ya sanya mutane da dama su ka rika kalubalantar sa da hakan.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!