Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

UN:Ta nuna damuwarta game da farfadowar Boko haram

Published

on

Majalisar dinkin duniya ta nuna damuwarta game da sake farfadowar mayakan Boko-Haram a yankin arewa maso gabashin kasar nan.

A cewar majalisar tun bayan da kungiyar Boko haram ta dawo da kaiwan hare-hare ta janye ma’aikatan ta na jinkai dari biyu da sittin, wanda ta ce hakan ya yi tasiri matuka wajen kara ta’azzara lamuran jinkai.

Majalisar ta kuma nuna damuwara game da Karin kwararar ‘yan gudun hijira wadanda ta ce ya zuwa yanzu wadanda suka isa garin Maiduguri daga Baga sun kai dubu talatin.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai magana da yawun majalisar dinkin duniya a Najeriya, Samantha Newport.

Sanarwar ta kuma ruwaito babban jami’in majalisar dinkin duniya a kasar nan Mr Edward kallon na cewa, akwai bukatan gwamnatoci da ke yankin tabkin Chadi su rika aiki tare don kawo karshen matsalar ba.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!