Labarai
Fasinjoji 26 ne suka samu raunika a hatsarin jirgin ƙasan Kaduna zuwa Abuja- NRC

Hukumar lura da sufurin jiragen kasa ta kasa NRC ta tabbatar da cewar fasinjoji 26 ne suka samu raunuka sakamakon hatsarin jirgin ƙasan da ya faru hanyar Kaduna zuwa Abuja a jiya Litinin.
Hukumar, ta bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da ta fitar a safiyar yau Talata a shafinta na X.
Haka kuma hukumar ta NRC, ta bayyana cewa baya ga fasinjojin da suka samu raunika akwai wasu daga cikin ma’aikatan jirgin da suka ji rauni
Sanarwar ta ce, shugaban hukumar, Kayode Opeifa, ya ce, hatsarin ya faru ne da misalin ƙarfe 9:16 na safe kusa da tashar Asham, inda aka ji ƙara mai ƙarfi lokacin da wani ɓangare na jirgin ya yi karo.
You must be logged in to post a comment Login