Connect with us

Labarai

FCET Bichi na shirin fara karatun Digiri na ƙashin kanta

Published

on

Kwalejin ilimi da fasaha ta gwamnatin tarayya da ke garin  Bichi a Kano, zata fara koyar da karatun Digiri na kashin kanta ba tare da haɗin gwiwa da kowacce jami’a ba.

Shugaban kwalejin fasahar ta Bichi dakta Bashir Sabo Abubakar, ne ya bayyana hakan jim kadan bayan da  tawagar gwamnatin tarayya karkashin hukumar da ke kula da jami’o’i Najeriya NUC suka kai ziyarar duba kayan aiki da malamai don sahale wa kwalejin fara yin karatun Digirin.

Dakta  Bashir Sabo, ya kuma  ce, ya na da kwarin gwiwar yin nasara wajen samar wa da al’ummar jihar kano ingantatcen ilimi idan hukumar ta  sahale musu fara gudanar da karatun na Digiri.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!