Connect with us

Labarai

Fiye da mutane Miliyan 2 ne kadai suka kammala yin rajistar zabe ta Internet- INEC

Published

on

Hukumar zaɓe ta kasa INEC ta ce daga cikin al’ummar kasar sama da miliyan 9 da suka fara yin rijistar katin zaɓe ta intanet, sama da miliyan 2 ne kawai suka kammala cika rajistar.

Hakan na kunshe a cikin sanarwar da mai magana da yawun hukumar Uwargida Victoria Eta-Messi, ta fitar da aka rabawa manema labarai.

Jami’ar ta ce jihar Osun ce kan gaba da ta fi kowa yawan sabbin masu rijista da lamba 200,251, sai jihar Kano da 151,604, kana Imo da 144,912 da kuma Sokoto da 141,526.

Jihohin da suka fi ƙaranci masu rijista sun haɗa da Ekiti da Abia da Ondo da Enugu da Ebonyi.

Hukumar ta INEC da masu sanya ido sun ce babban giɓin da ake samu na rashin cike rijistar shi ne mutane da dama na fara rijista amma ba sa samun damar kammala ɗaukar hoto da sauran bayanai.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!