Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Ganduje ya sakawa dokar kikiro masarautu hannu

Published

on

Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ya sakawa dokar  kirkiro masarautu hannu.

Gwamanan ya sakaw dokar hannu a dakin taro na coronation a gidan gwamnatin Kano.

Gwamnan ya sakawa dokar hannu  bayan majalisar dokoki ta amince da dokar.

Da yake jawabi bayan sa hannu  Gwamna Ganduje yace dokar  kirkiro masarautun an yi ta ne domin kawo cigaba ga al’ummar yankunan sababbin masarautun.

A dai ranar 8 ga watan  Mayu na shekarar 2019 ne tsohuwar majalisar dokokin ta jahar Kano ta amince da dokar kirkiro karin masarautu a Kano da suka hada da Karaye  da Rano da Bichi da Gaya.

Amma a ranar 21 ga watan Nuwambar  da ya gabata ne babbar kotun  Kano ta soke kirkirar masarautun .

Dalilin da ya sa kenan gwamna Ganduje ya sake aike dokar domin amincewa da ita bisa kaida.

 

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!