Connect with us

Labarai

Garba Shehu ya ƙaryata Jonathan kan kalamansa ga Buhari

Published

on

Tsohon mai bai wa marigayi shugaba Muhammadu Buhari shawara a harkokin yaɗa labarai Garba Shehu, ya karyata iƙirarin tsohon Shugaban ƙasa Goodluck Jonathan cewa, ƙungiyar Boko Haram ta taɓa naɗa Buhari a matsayin wanda zai jagoranci tattaunawar sulhu tsakaninsu da Gwamnatin Tarayya.

Garba Shehu ya yi wannan raddi ne a cikin wata sanarwa da ya fitar mai taken “Boko Haram ba su taɓa naɗa Buhari a matsayin mai shiga tsakani ba.”

Wannan martani na Garba Shehu, ya biyo bayan jawabin Jonathan a wajen kaddamar da littafin “Scars” da tsohon Hafsan Sojojin Najeriya, Janar Lucky Irabor mai ritaya ya rubuta.

A wajen taron, tsohon shugaban ya ce, a wani lokaci da gwamnatinsa ta kafa kwamitoci, mayakan Boko Haram sun ambaci Muhammadu Buhari a matsayin mutumin da suke so ya jagoranci tattaunawa da gwamnati.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!