Connect with us

Labarai

Gidaje 200 zuwa 300 ne ke rushewa a Najeriya duk shekara- COREN

Published

on

‎Majalisar kula da ayyukan Injiniyoyi ta kasa COREN ta ce zata rufe duk wani guri da ake aikin daya saba dokar ta tare da mika Injiniyan a gaban Kotu domin dakile illar rushewar Gine – Ginen dake sanadin mutuwar al’ummar kasa.

‎Shugaban Majalisar Injiniya Farfesa Sadik Zubair Abubakar, ne  ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da Majalisar ta COREN ta gudanar a nan Kano.

‎Shugaban ya ce, shekaru 53 kenan da kafa COREN amma kwalliya bata biya kudin Sabulu ba, domin a iya Abuja majalisar take aiki wanda hakan yasa suke so su rika yin aiki a kowacce jiha a Najeriya a halin yanzu.

‎Ya kara da cewa a binciken da COREN ta gudanar ta gano cewa kimanin gidaje dari biyu zuwa dari uku ne suke rushewa a Najeriya a duk shekara a don haka ya zama wajibi a sauya wannan tsari.

‎                                     

‎Majalisar ta bada lambar waya da mutane zasu kwarmata duk wani aikin Injiniya da suka gano ana tafka Almundahana kuma za a bada kyauta ga masu kwarmata wa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!