Connect with us

Labarai

Gwamna Abba Kabir ya sanya hannu kan dokar samar da karin hukumomi 4

Published

on

Gwamnan Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya sanya hannu kan dokar samar da wasu sabbin hukumomi guda huɗu.

Babban daraktan yaɗa labaran gwamnan Sunusi Bature Dawakin Tofa, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwar da ya fitar da safiyar yau Juma’a.

Sanarwar, ta ce za a samar da sabbin hukumomin ne domin kara inganta hanyoyin da za su samar wa jihar Kano ci gaba.

Sabbin hukumomin da gwamnan ya amince da samar wa sun hada da, Hukumar bayar da kariya ta jihar da Hukumar kula da Alluna da kuma tallace-tallace sai hukumar yada labarai da bunkasa fasahar sadarwa da kuma Hukumar bunkasa kanana da matsakaitan masana’antu

Haka kuma, a cewar sanarwar sanya hannu kan dokar samar da sabbin hukumomin na cikin yunƙurin gwamnatin na sabbin dabarun da za su tallafa wa kananan sana’o’i da tsaftace harkokin tallace-tallace domin bai wa al’umma kariya da kuma inganta bangaren.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!