Connect with us

Labarai

Gwamna Abba ya sha alwashin ci gaba da inganta rayuwar ma’aikata

Published

on

Yayin da ake gudanar da bikin ranar ma’aikata a yau Alhamis, Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sha alwashin ci gaba da inganta rayuwar ma’aikata tare da samar musu da yanayin aiki mai kyau.

Gwamna Injiniya Abba Kabir Yusif, ya bayyana hakan ne yayin bikin ranar ma’aikata na bana da aka gudanar yau Alhamis a filin wasa na Sani Abacha da ke Kofar mata.

Gwamnan, ya kuma ce gwamnatinsa ta mayar da hankali wajen horas da ma’aikata tare da samar musu da kayan aiki dai-dai da zamani.

A nasa jawabin, shugaban kungiyar Kwadago ta ƙasa NLC reshen jihar Kwamared Kabiru Inuwa, kira ya yi ga gwamnan kan ya cika alkawarin da ya dauka na gina dakin taro a sakatariyar kungiyar tare da sanya sunan marigayi tsohon gwamna Alhaji Muhammadu Abubakar Rimi.

Yayin taron, wanda ya samu halartar kungiyoyin ma’aikata da dama da suka hadar da na gwamnati da masu zaman kansu, an karrama wasu cikin kungiyoyin ma’aikatan da suke bada gudunmawa a hukumomin da suke aiki cikin su harda kungiyar ma’aikatan kananan hukumomi NULGE.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!