Connect with us

Labarai

Gwamna Abba ya sha alwashin hukunta waɗanda ke da hannu a rasuwa Inuwa Sharada

Published

on

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sha alwashin daukar mataki mai tsanani kan duk wanda aka samu da hannu kan zargin mutuwar shugaban rundunar masu yaƙi da kwacen Waya marigayi Inuwa Sharada, wanda ya rasu a Larabar makon nan.

Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya bayyana hakan ne yau Alhamis yayin gudanar da jana’izar marigayi Inuwa Sharada, inda ya bayyana rashin sa a matsayin abin takaici da kuma nuna rashin imani da tausayi.

Gwamna Abba ya ce, gwamnati ba za ta lamunci irin wannan abu ba, musamman ganin irin rawar da marigayin ke takawa wajen taimaka wa hukumomin tsaro da gwamnati wajen tabbatar da zaman lafiya a cikin al’umma.

Gamnan ya kuma jajanta wa iyalan marigayin da abokansa, ƴa na mai tabbatar da cewa, gwamnatin jihar Kano za ta ci gaba da tallafa musu tare da tabbatar da cewa irin wannan lamari bai sake faruwa ba a nan gaba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!