Connect with us

Labarai

Gwamna Fubara ya nemi haɗin kan al’ummar Rivers

Published

on

Gwamnan jihar Rivers Siminalayi Fubara ya buƙaci al’ummar jihar da su ba shi haɗin kai wajen ciyar da jihar gaba ba tare da la’akari da bambancin siyasa ko addini ko ƙabilanci ba.

 

Gwamnan, ya buƙaci hakan ne yayin da ya ke jawabi ga al’ummar jihar a birnin Fatakwal.

 

Haka kuma, gwamna Fubara, ya gode wa Shugaba Tinubu bisa ƙoƙarin da ya ce ya yi wajen sasanta rikicin siyasar jihar.

 

A ranar Laraba ne Shugaba Tinubu ya sanar da kawo ƙarshen wa’adin dokar ta-ɓaci da ya sanya wa Rivers ta tsawon wata shida, sakamakon rikicin siyasar jihar da ya ƙi-ci-ƴa-ƙi-cinyewa.

 

Gwamnan ya ce a tsawon wata shidan da jihar ta ɗauka ƙarƙashin dokar, Tinubu ya yi ƙoƙarin sasanta duka ɓangarorin.

 

Fubara ya kuma ce, a yanzu shi da duka sauran ƴansiyasar jihar sun sanya jihar da muradunta a gaba domin ciyar da Rivers gaba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!