Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnan Jihar Borno ya kai ziyara asibitin kwararru na Umaru Shehu

Published

on

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya kai ziyarar ba zata da safiyar jiya Talata a asibitin kwararru na Umaru Shehu dake birnin Maiduguri.

 

Babagana Zulum wanda ya bayyana takaicin sa ganin yadda babu wani likita koda guda daya dake bakin aikin sa a cikin asibitin a yayin zaiyarar ba zatar, sai dai ma’aikatan jinya da masu kula da marasa lafiya.

 

Rahotanni sun bayyana cewar gwamnan na Borno yayi kokarin kiran wasu daga cikin likitocin ta wayar tarho amma babu wanda ya daga.

 

Haka zalika Babagana Zulum ya bayyana rashin gamsuwar sa kan yadda ake kula da marasa lafiya a asibitin.

 

Kafin barin sa asibitin Gwamnan na jihar Borno ya bada umarnin da a baiwa babban daraktann asibitin takardar tuhuma da yayi bayani kan mai haddasa rashin likitoci a asibitin na Umaru Shehu.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!