Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

NAHCON: mutane 5 sun rasa rayukansu a aikin hajjin bana

Published

on

Hukumar dake kula da aikin hajjin ta kasa NAHCON Ta tabbatar da mutuwar ‘yan Najeriya 5 a kasa mai tsarki a yayin aikin hajjin bana

 

Shugaban ayarin likitoci a kasa mai tsariki Dr, Ibrahim Kana ne ya bayyana hakan cikin sanarwar da ya fitar a birnin Madina cewar hukumar aikin hajji ta kasa ta sami rahoton mutuwar alhazai 5 a Saudiya.

 

Dr, Ibrahim Kana ya ce wadanda suka rasun akwai mata 3 da maza 2, kuma mutum guda ne ya rasu a birnin Madina yayin da sauran 4 suka rasu a birnin Makkah

 

A cewar sanarwar mutanen sun rasa rayukan su a sakamakon cutattuka daban-daban da suka hada da cutar zuciya da ta huhu da dai sauran su.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!