Connect with us

Labarai

Gwamnan Jihar Kano ya ƙaddamar da biyan kuɗaɗen garatuti ga tsoffin kansiloli 1,371

Published

on

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya ƙaddamar da biyan kuɗaɗen garatuti ga tsoffin kansiloli 1,371 da suka yi aiki a lokacin tsohuwar gwamnati a karo na uku.

Da ya ke ƙaddamar da shirin a yau Laraba, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa matakin na daga cikin ƙudirin gwamnatinsa na cika alƙawura da kuma tabbatar da adalci ga shugabannin ƙananan hukumomi da suka taɓa hidimta wa al’umma a matsayin shugabanni.

Gwamna Abba ya kuma jaddada cewa tsoffin Kansilolin sun bayar da gagarumar gudunmawa wajen tafiyar da harkokin ƙananan hukumomi da bunƙasa ci gaban al’umma.       

A cewar gwamnan, wannan shi ne karo na uku da Ya ke biyan garatuti ga tsoffin kansiloli, kuma gwamnatinsa za ta ci gaba bin wannan tsari har sai an kammala biyan dukkan waɗanda suka cancanta a faɗin ƙananan hukumomi 44 na jihar Kano.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!