Connect with us

Labarai

Gwamnan jihar Neja ya tabbatar da ceto ƙarin ɗalibai 11 na makarantar St Mary da yan bindiga suka sace

Published

on

Gwamnan jihar Neja Umar Bago ya tabbatar wa manema labarai cewa, jami’an tsaro sun ceto ƙarin ɗalibai 11 na makarantar St Mary da yan bindiga suka sace.

Gwamnan, ya bayyana cewa, an samu nasarar ceto daliban 11 ne a wani aiki na haɗin gwiwa tsakanin sojoji da yan sa kai inda aka gano yaran a wata gona

Sai dai gwamnan bai bayyana hanyoyin da aka bi wajen tantance waɗanda aka kuɓutar din ba, inda ya musanta cewa an sace yara sama da 300.

Haka kuma, ya ce, makarantar ba ta bayar da bayanan da za a iya dogara da su ba, kuma sun buɗe makarantar ne duk da gargaɗin da jami’an tsaro suka yi.

Gwamna Bago ya kara da cewa, gwamnatinsa ta buɗe wata rijista a ƙaramar hukumar Agwara domin iyaye su rubuta sunayen ƴaƴansu da suka ɓata sakamakon harin, amma zuwa yanzu iyaye 14 kacal ne suka rubuta.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!