Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnan jihar Ondo ya kori kwamishinonin 3 a gwamnatinsa

Published

on

Gwamnan jihar Ondo Oluwarotimi Akeredolu ya sanar da cewar ya kori kwamishinonin 3 dake kunshin gwamnatin sa yayin da nada wasu mutum 5 a matsayin sababbin kwamishinoni.

Wannan na kunshe cikin sanarwar da sakataren yada labarai ga gwamnan Mr Olusegun Ajiboye ya fitar a birnin Akure.

Sanarwar ta sanar da sunayen sababbin kwamishinonin da gwamnan Akeredolu ya nada sun hada da Mrs Yetunde Adeyanju da Mrs Titilayo Adeyemi da Mr Temitayo Oluwatuyi da  Mr Fatai Olotu da kuma Mr Akindotun

Haka zalika a cewar sanarwar gwamnan jihar ya ce daukar matakin ya zama wajibi wajen yin tankade-da rera, saboda gwamnatin sa na bukatar jajirtattu da za su baiwa jihar ta Ondo gudunmawa.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!