Connect with us

ilimi

Gwamnati Sokoto ta gargaɗi shugabannin Makarantun Sakandire

Published

on

Gwamnatin jihar Sokoto ta gargaɗi Shugabannin Makarantun Sakandire kan su guji karɓar ƙudi a hannun ɗalibai da sunan kuɗin jarrabawa.

 

Wanann na cikin sanarwar da Kwamishinan Ilimi na jihar Farfesa Ahmad Ladan Ala ya fitar.

 

Sanarwar ta ce, maʼaikatar ilimi ta samu ƙorafe-ƙorafe cewa wasu ʼPrincipalsʼ na karɓar kuɗaɗe daga wajen ɗalibai kafin basu damar rubuta jarrabawa.

Ya ce, wannan babban laifi ne, domin gwamnan jihar ya riga ya biya dukkan waɗannan kuɗaɗe.

 

Sanarwar ta buƙaci iyaye da ɗalibai su kai rahoton duk makarantar da aka bukaci su bada kuɗi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!