Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da shirin tudun mun tsira ga waɗan da suka tuba daga harkar daba

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ƙaddamar da shirin tudun mun tsira ga dukkanin waɗan da suka tuba daga harkar daba a faɗin jihar kano domin tabbatar da an tsaftace jihar daga duk wani tashe tashen hankali da yake da nasaba da harkar faɗan daba da sace-sace.

Gwamnan jihar kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ne ya ƙaddamar da shirin a yau domin tattaunawa da dukkanin shugabannin waɗan da suka ajiye makaman su daga harkar daba, domin kare jihar kano daga dukkanin wani tashe tashen hankula da suke addabar jihar.

Gwamnan Abba Kabir Yusuf wanda ya samu wakilcin Kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kwamrat Ibrahim Abdullahi Waiya ya ce Gwamnatin kano ta gama shiri tsaf ƙarƙashin hukumar ƴan sanda ta jihar wajen tantance dukkan wadan da suka tuba ta yadda za’a samar musu da aikin yi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!